Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kungiyar Arsenal Ta Shirya Siyo 'Yan-wasa

Zaben 'Yan-wasa Na kwarai Yazama Dole
Zaben 'Yan-wasa Na kwarai Yazama Dole

Koch na kungiyar kwallon kafar Arsenal, yace sayo dan wasa ba abu ne me sauki ba kamar yadda ake gani.

Shugaban kungiyar Mr. Arsene Wenger a shirye yake don bude kofar saye da siyarwar yan wasa a watan Janairu, ya kuma yadada cewar dole yayi tunani wajen zabe.

Don ‘yan wasa masu rauni sunyi yawa a tawagar kungiyar ta Mr. Wenger, wanda dan wasa Mesut Ozil na fama da ciwon Guywa, Jack Wilshere na fama da idon kafa, Mikel Arteta na fama da ciwon kafa , Yaya Sanogo na fama da ciwo a cinyar shi, shi kuma Mathieu Debuchy na fama da ciwon idon kafa, da dai sauransu.

A kwai dai alamun kungiyar ta Arsenal nashirin motsi a watan Janairu, wanda take ta 8 a wasan firimiya Lig bayan rashin nasara na baya-da-baya.

please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:00:44 0:00
Shiga Kai Tsaye


  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

XS
SM
MD
LG