Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kungiyar Izala ta Kashe Kimanin Naira Miliyan 60 Kan 'Yan Gudun Hijira


Shugaban kungiyar Izalatul Bidi'a Wa Iqamatis Sunnah ta Najeriya, Sheikh Abdullahi Bala Lau
Shugaban kungiyar Izalatul Bidi'a Wa Iqamatis Sunnah ta Najeriya, Sheikh Abdullahi Bala Lau

Kungiyar Izalatul bidi'a wa Iqamatis sunnah, ta jihar Bono, ta raba kayayyakin abinci, ga ‘yan gudun hijira fiye da dubu goma sha shida, da rikicin Boko Haram, ya raba da gidajensu, wadanda ke saune a gidajen mutane daba-daban a fadi jihar Borno.

Kungiyar tace ta dauki wannan matakin ne don rage wahalhalun da jama’a, ke fuskanta, masamman ma wadanda ke rike da ‘yan gudun hijira, a gidajensu.

Imam Baba Kura Gwani, wanda yake shine Mataimakin shugaban majalisar Malamai yace kungiyar, ta kashe kimamin Naira miliyan 60 wajen sayen kayyakin abinci, don tallafawa ‘yan gudun hijiran.

Wasu daga cikin wadanda suka amfana da tallafin sun yabawa kungiyar, da cewa taimakon zai tamaka wajen sauka masu kuncin rayuwa.

Kungiyar Izala - 3'23"
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:23 0:00

XS
SM
MD
LG