Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ma'aikatan Tsaro Amurka Zata Sanar da Majalisar Dokoki Kafin A Kaiwa Syria Hari


Sakataren Tsaron Amurka Jim Mattis
Sakataren Tsaron Amurka Jim Mattis

A lokacin da shugaban Amurka ke neman yadda zai yi da batun Syria sakataren tsaron kasar yace zai sanar da majalisar dokoki duk halin da ake ciki

Ahalinda ake ciki kuma, sakataren tsaron Amurka Jim Mattis, yayi alkwari jiya Alhamis, cewa, ma'aikatar tasaron Amurka da ake kira Pentagon, zata "sanarwa" majalisar dokoki duk wani shirin daukar matakin soja akan Syria, kasar da Amurkan take nazarin daukar matakin soja da nufin ladabtarda gwamnatin kasar kan hari da aka kai da makamai masu guba.

Amma abun lura, sakataren na tsaron Amurka bai ambaci batun neman izinin majalisa kamin daukar matakin sojin ba, wadda Amurkan zata auna kan gwamnatin kasar ta sham ko Syria karkashin jagorancin Bashar al-Assad.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG