Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Madugun 'Yan Tawayen Sudan Ta Kudu Ya Koma Kasar


Reik Machar ya isa Juba
Reik Machar ya isa Juba

A karon farko cikin shekaru biyu madugun ‘yan tawayen Sudan ta Kudu Riek Machar ya koma babban birnin kasar.

Machar ya isa birnin da safiyar jiya Laraba ta filin saukar jiragen sama na Juba, daga kasar Afirka ta Kudu domin ya halarci wani buki da abokin hamayyarsa Salva Kiir ya shirya.

Mutanen biyu dai sun sabunta yarjejeniyar sulhu da suka rattabawa hannu tun watan Satumba, don kawo karshen rikicin kasar da ya kwashe kusan shekaru biyar.

Machar dai ya taba zama mataimakin shugabanSalva Kiir bayan samun ‘yancin kai da kasar tayi daga Sudan a shekarar 2011, amma daga baya giyar mulki ta yi sanadiyar fada tsakaninsu da ya bayansu. Kiir da Machar dai sun yi ta sa hannu akan yarjeniyoyin sulhu barkatai, amma ba a cimma nasara ba. ciki har da ta shkearar 2016 wadda a sanadin barkewar tashin hankali a babban birnin Machar ya bar kasar.

Yakin basasar kasar yayi sanadiyar mutuwar kusan mutane 400,000 yayin da miliyoyi suka rasa muhallansu.

Karkashin sabuwar yarjejeniyar Machar zai rike mukamin mataimakin shugaban kasa na farko karkashin gwamnatin wucin gadi.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG