Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mahukuntan Poland Sun Bukaci Amurka Ta Kafa Sansanin Sojojinta A Kasarsu


Wasu sojojin Amurka dake kasar Poland a yanzu
Wasu sojojin Amurka dake kasar Poland a yanzu

A kokarin tsoratar da Rasha domin kada ta mamaye kasarsu, mahukumtan kasar Poland sun bukaci Amurka ta kafa sansanin sojojinta a kasarsu kamar yadda ministan tsaron kasar ya sanar

Kasar Poland ta bukaci jami’an Amurka da su kafa rundunar sojoji tare da zuba dubban dakarun Amurka, a wani mataki na tsorartar da Rasha.

A jiya Litinin, Ministan tsaron kasar, Marius Blaszczak, ya ce a kwanakin nan ya tattauna da hukumomin Washington kan yadda za a kafa matsugunin sojin Amurka na dindindin a kasar ta Poland.

“Wannan kasancewa ta dakarun Amurka a kasar, na da matukar muhimmanci wajen jefa tsoro a zukatan abokanan hamayya, Inji Minista Blaszczak yayin wata hira da ya yi da kafar Radio 1.

Kasar Poland ta jima tana nuna damuwa kan harkokin tsaro a yankin, tun bayan da Rasha ta mallake yankin Crimea daga Ukraine a shekara 2014.

A can birnin Moscow, Kakakin shugaban Rashan, Vladimir Putin, Dmitry Peskov, ya ce, tura karin dakarun yammaci a kusa da kan iyakokin Rasha, “ba zai kara komai ta fuskar tsaro da zaman lafiya a nahiyar ba.”

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG