Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Majalisar Dinkin Duniya Ta Damu da Hukuncin Masar


Magoya bayan hambararen shugaba Morsi.
Magoya bayan hambararen shugaba Morsi.

Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana damuwar majalisar dangane da hukuncin kisan da kasar Masar ta yiwa magoya bayan kungiyar 'yanuwa Musulmai.

Baban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Banki Moon ya baiyana damuwa akan rahotanin dake cewa, wata kotun kasar Masar ta yankewa magoya bayan haramtattaciyar kungiyar Muslim Brotherhood hukuncin kisa.

A wata sanarwar daya gabatar jiya Litinin, Mr. Ban yace a filli ne cewa babu alamar anyi adalci a hukuncin da aka yanke.

Itama Amirka tace ta damu da wannan hukunci. An dangata shari'ar da aka yi musu da mumunar tarzomar data barke a Minya da wasu wurare a Masar, bayan da jami'an tsaro da karfin tsiya suka tarwatsa zanga zangar da magoya bayan kungiyar Muslim Brotherhood suka yi a watan Augustan bara.

Kungiyar Muslim Brotherhood ta gabatar da wannan sanarwa dake cewa zata ci gaba da amfani da hanyoyin lumana wajen kawo karshen mulkin soja a kasar.
XS
SM
MD
LG