Shirin dokar na neman a tanadi kudi sama da dala biliyan 4 daga kudaden da aka ware na agajin gaggawa don agazawa bakin hauren da aka tsare, musamman yara.
Kuri’ar da aka kada inda ‘Yan majalisa 84 suka amince da dokar wasu su 8 kuma suka ki, na zuwa ne a daidai lokacin da ake cigaba da sa ido akan yadda gwamnatin Trump ke kula da masu kananan shekaru, a yayinda kuma mutuwar wani mutum dan kasar El Salvador da diyarsa a lokacin da suka yi kokarin tsallaka rafin Rio Grande zuwa Amurka ya janyo suka sosai.
“Babu tantama yanayin da ake ciki a kudancin iyakar kasarmu babban tashin hankali ne ta fuskar taimakon agajin jinkai da tsaro,” a cewar Sanata Richard Shelby na jam’iyyar Republican daga jihar Alabama, ya kuma ce babu dalilin da zai sa a yi jinkiri wajen daukar mataki.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 04, 2023
Amurka Ta Kakkabo Babban Balan-Balan Na Leken Asirin China
-
Janairu 25, 2023
Mawakiya Yar Najeriya Ta Yi Tarihi A Bikin Bada Lambar Yabo Na Oscar
-
Janairu 13, 2023
Lisa Marie Presley, Diyar Mawaki Elvis Ta Rasu
-
Janairu 11, 2023
Ana Tsaftace Yankunan Da Mahaukaciyar Guguwa Ta Ratsa A California
Facebook Forum