Malaman addinin Islama daga Afghanistan, da Pakistan,da Indonesia, sun jaddada cewa hare haren kunar bakin wake a Afghanistan dama a yankin baki daya- haramun ne kuma ya sabawa manufofin addinin islama. Malaman sun bayyana hakan a dai dai lokacinda suka hallara domin taron wuni-daya a Bagor a Indonesia, da zummar tattaunawa kan tarzomar da take ci a Afghanistan.
Taron da aka yi ranar Jumma'a,yazo ne watanni bayan da malaman Pakistan su fiyeda dubu daya da dari takwas, suka yi fatawar da take Allah wadai da ta'addanci ta ko wace fuska a kasar.
Afghanistan, ta soki fatwar ta Pakistan, domin ta yi Allah wadai ne ga ta'addanci a Pakistan kadai. Taron da ake yi a Bogor, an hada harda malaman Pakaistan ne, domin ana ganin suna da tasiri kan kungiyoyin mayakan sakai dake Pakistan.
Ahalinda ake ciki kuma,'Yansanda a Indonesia sun ce, 'yan kunar bakin wake sun kai hari kan majami'u ukua a birnin Surabaya dake tsibirin Java. Jami'ai suka ce akalla mutane biyu sun mutu, wasu 13 suka jikkata.
Facebook Forum