Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Manyan Ma'aikatan Jami'o'i A Najeriya Sun Fara Zanga-Zangar Lumana


Yajin aikin ma'aikatan jami''o'i zai shafi bangarori da dama na tattalin arzikin Najeriya.

Kungiyar ma'aikatan Jami'o'i tare da hadin gwiwa kungiyoyin manyan ma'aikatan jami'o'i SSANU, da kuma kungiyar JAC kungiyar da ba na ilimi ba, sun dau matakin fara zanga-zangar lumana, don nuna rashin gamsuwar su da wasu abubuwa guda 8.

Kamar yadda shugaban kungiyar NASU na Jami'ar Kimiyya da Fasaha ta Wudil a jihar Kano, Nura Mohammed ya zayyana, sun shiga yarjejeniya da Gwamnatin tarayya tun a shekarar 2009, wadanda su ka hada da rashin dai-daiton biyan kudin albashi na IPPIS, da batun biyan kudin alawus-alawus na ma'aikatan.

Kana da bashin da ma'aikatan ke bi na karin albashi da gwamnati ta yi, akwai batun sabunta yarjejeniyar da gwamnati ba ta yi ba bayan shekara biyar.

Haka sai batun fansho na ma'aikata da suka bar aiki, kana da yadda ba'a kula da Jami'o'i mallakar Jihohi, da bukatar kafa kwamiti na musamman da zai rika ziyarar ganin ayyukan jami'o'i da gwamnati ba ta yi, inda ya ce yin haka ba dai-dai ba ne. Wadannan da ma wasu dalilai ne suka sa su daukar wannan matakin.

Nura Mohammed, ya ce gwamnati ta na fifita kungiyar Malaman Jami'o'i akan ma'aikatan jami'o'in, saboda haka suna neman a dai-daita sahu.

Shi kuwa wani Malami a tsangayar Ilimi ta Jami'ar Abuja Dr. Usman Abdullahi Manu, ya yi bayanin cewa, idan har wadannan ma'aikatan suka shiga yajin aiki, to fa zai shafi Malaman Jami'o'in sossai, domin su ne masu ayyukan shirya albashin Malaman da sauran ayyukan gudanar da jami'o'in.

Dr. Manu yana mai ba gwamnati shawarar cewa, ta yi maza ta taimaka wa bangaren ilimi, idan ana so kasa ta ginu saboda ilimi shi ne ginshinkin cigaba a ko ina cikin duniya.

Ga rahoton Medina Dauda ta hada a cikin sauti.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:43 0:00

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG