Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Manyan Kasashen Yammacin Turai Zasu Goyi Bayan Sabuwar Gwamnatin Libya - Kerry


Sakataren harkokin wajen Birtaniya Philip Hammond da Sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry a taron da suka yi jiya Litinin a Vienna
Sakataren harkokin wajen Birtaniya Philip Hammond da Sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry a taron da suka yi jiya Litinin a Vienna

Manyan kasashen duniya sunce zasu goyi bayan sabuwar gwamnatin kasar Libya a wani yunkurin ganin Majalisar Dikin Duniya ta dage takunkumin data azawa kasar.

Suna ganin matakin zai taimakawa gwamnatin Libyan ta dakile barazanar matakan tsaron cikin gida da kuma yaki da 'yan kungiyar ISIS.

Sakataren Harkokin Wajen Amurka John Kerry shi ne ya bada sanarwar wannan shawara bayan wani taron da Amurka da Italiya suka yiwa jagoranci.

Mr. Kerry yace Amurka da manyan kasashen yammacin turai ashirye suke su baiwa sabuwar gwamnatin Libya taimakon jin kai da na tattalin arziki da kuma matakan tsaro tare da kayan yaki.

Sabuwar gwamnatin da aka kafa a Libya tana fuskantar kalubale daga kungiyoyin dake gaba da juna a cikin kasar da kuma 'yan yakin sa kai da suke da alaka da kungiyar ISIS, wadanda suka kafa sansani a birnin Sirte, kuma sun yi anfani da sansanin wajen kaddamar da hare-hare akan kasar Tunisia makwafciyar Libya.

Sabon Firatim Ministan Libya da John Kerry a taron jiya
Sabon Firatim Ministan Libya da John Kerry a taron jiya

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG