Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mataimakin Babban Sifeton 'Yansada Ya Kira Gwamnatin Ogun Ta Kafa Hukumar Dakile Kwace Filaye


Ibrahim Idris, Babban Sifeton 'Yanasandan Najeriya
Ibrahim Idris, Babban Sifeton 'Yanasandan Najeriya

Mataimakin babban sifeton 'yansandan Najeriya mai kula da jihohin Ogun da Legas Adamu Ibrahim ya kira gwamnatin Ogun ta kafa wata hukuma da zata kula da dakile harkokin masu magudin kwace filayen jama'a

Adamu Ibrahim mataimakin babban sifeton 'yansandan Najeriya ya kira gwamnatin Jihar Ogun da ta kafa wata hukuma ta musamman da zata takawa masu magudin kwace filayen jama'a birki tare da hukumtasu.

Mataimakin ya bada shawarar ce yayinda ya kai wa gwamnan Ogun Ibikunle Amosun ziyara a ofishinsa dake Abeokuta babban birnin jihar. A cewarsa hukumar zata takawa masu yaudarar mutane suna kwace masu filaye birki. Yawancin masu yin hakan daga jihohin dake makwaftaka da Ogun suke fitowa.

Inji Adamu Ibrahim masu magudin kwace filaye suna shirin kwararowa jihar amma idan aka kafa hukumar da zata dauki matakai a kansu, zasu yi takatsantsan saboda hukumar zata hanasu cin karensu babu babbaka.

Mataimakin babban sifeton ya mika kokon bararsa ga gwamnatin jihar inda ya bukaci a sayawa 'yansandan jihar jiragen ruwa masu bindigogi da zasu dinga anfani dasu kan rafuka da ke jihar tare da tekun dake bangaren jihar domin shawo kan masu aikata laifuka.

Gwamnan jihar Ibikunle Amosun ya ce gwamnatinsa zata taimakawa rundunar 'yansandan da kayan aiki saboda suna aiki da jama'ai da shugabannin 'yansandan. Shi ma gwamnan ya nemi taimakon 'yansandan kan masu aikata aika aika kan ruwa a cikin jihar.

Ga rahoton Hassan Umaru Tambuwal da karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:39 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG