Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Matsalar Manoma a Arewa Maso Gabas


Kayayyakin noma zuben a hedkwatan ma’aikatan aikin gonar jihar, Borno a Maiduguri, 26, ga Mayu 2014.
Kayayyakin noma zuben a hedkwatan ma’aikatan aikin gonar jihar, Borno a Maiduguri, 26, ga Mayu 2014.

A cikin makonnin dai al-ummomi da dama ne suka samu komawa yankunansu da aka kwato daga mayakan Boko Haram.

To sai dai da alamun wadannan al-ummomin yanzu haka ana fama da matsaloli da dama. Domin bayan muhallansu da aka lalata, da rashin asibitoci, da makarantu da kuma gadojin da aka dasa wa nakiyoyi, wata matsala da al-ummomin yankin ke fuskanta a yanzu itace ta rashin abinci, yayin da wasu ke tsoron fara aikin gona, duk da cewa damina na kankama.

Wani mazaunin yankin wanda ya so a sakaye sunanshi cewa yayi “ka san cewa wannan abun da tsoro ne, domin sun daddasa nakiyoyi cikin wadannan gonaki, kuma in ka shiga gonarka sai ka je ka ga gawa. Zaka ga kasusuwa ya rube wanda ba’a binne ba. Kuma irin wannan akwai hatsari.

Da yake karin haske, wani masani a harkar noma Alhaji Musa Yakubu yayi gargadin cewa “kaga kwanakin baya ta wajen Maiha da sauransu an samu bom ya fashe. To irin wadannan abubuwan jama’a da yawa suna tsoro. Kuma wani lokaci kana tafiya a cikin daji ka ga bindiga, kaga gawar da ta lalace”.

To sai dai kuma ita sabuwar gwamnatin jihar Adamawan ta sha alwashin magance wadannan matsaloli da al-ummomin ke fuskanta.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:31 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG