Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ministan Sharaar Amurka Jeff Session Yace A shirye Yake Ya bada Bayani Gaban Majilisar Dokokin Amurka


Attorney General Jeff Sessions speaks at a news conference after touring the U.S.-Mexico border with border officials, April 11, 2017, in Nogales, Ariz. Sessions announced making immigration enforcement a key Justice Department priority.
Attorney General Jeff Sessions speaks at a news conference after touring the U.S.-Mexico border with border officials, April 11, 2017, in Nogales, Ariz. Sessions announced making immigration enforcement a key Justice Department priority.

Atoni Janar kuma ministan shari'a na Amurka Jeff Sessions, ya gayawa majalisar dokokin Amurka cikin wasika da ya rubuta mata ranar Asabar cewa, a shirye yake ya bayyana a gaban kwamitin kula da harkokin leken asiri

Wadda ke binciken katsalandan ko kusten da Rasha tayi a zaben shugaban kasa da aka yi anan Amurka a bara. Ana sa ran Sessions zai amsa tambayoyi kan batutuwa da suka taso game da shi a makon jiya, lokacinda tsohon darektan hukumar FBI James Comey, ya bayyana a gaban kwamitin.

Sessions ya tsame hanunsa daga dukkan al’amurran da suka jibanci binciken da ma'aikatar shari'a wacce take karkashinsa take gudanarwa kan zargin take-taken na Rasha lokacin zaben, domin yana daga cikin jami'an kwamitin yakin neman zaben Trump, da suka gana da jakadan Rasha a Amurka gabannin zaben.

A cikin watan Janairu lokacinda ya bayyana domin a tantance shi zama ministan shari'a. Da yake amsa tambayar da senata Al-Franken dan Democrat mai wakilatar jahar Minnesota ya yi masa, Sessions yace bai gana da wani jami'in kasar Rasha ba a lokacin yakin neman zaben na Amurka

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG