Yau Laraba 8 ga watan Afirilu gobara ta kona wasu sassan ofishin babban Akawun gwamnatin tarayyar Najeriya dake birnin Abuja, amma bayan sa’a daya an sami nasarar shawo kan gobarar.
A wata hira da Muryar Amurka ta yi da babban Akawun gwamnatin Najeriya Ahmed Idriss, ya ce na’urar sanyaya daki ce ta haddasa gobarar amma an sami nasarar kashe ta ba tare da ta yi wata babbar barna a muhimman wurare ko na’urori na tattara bayanan sirri akan kudaden gwamnatin tarayyar Najeriya ba.
Idriss ya kuma ce ayyukansu basu tsaya ba kuma an yi gyare-gyaren da suka kamata.
Tuni dai wasu suka fara zargin ko da gangan aka tada gobarar da nufin yin rufa-rufa ko boye wani sirri na kashe kudaden gwamnati, musamman a lokacin da masu hali ke bada kudaden tallafi ga gwamnati don yaki da cutar COVID-19.
Da yake maida martini game da zargin, Idriss ya ce jama’a na da damar fadin albarkacin bakinsu, amma kudin gwamnati ba a ofishinsu suke ba, suna ajiye ne a babban bankin Najeriya na CBN. Kaddara ce kawai ta faru, a cewarsa.
Saurari karin bayani cikin sauti daga Umar Faruk Musa.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 25, 2021
Tattaunawar Gumi Da 'Yan Ta'adda Ba Alheri Ba Ne - Dattawan Arewa
-
Fabrairu 25, 2021
An Yi Jana’izar Sojojin Najeriya Da Suka Mutu a Hatsarin Jirgin Sama
-
Fabrairu 25, 2021
Ba Mu Da Abincin Da Zamu Ciyar Da 'Yan Makarantar Kagara- ‘Yan bindiga
-
Fabrairu 25, 2021
Takaddama Na Zafafa Tsakanin Gwamnan Bauchi Da Na Benue
-
Fabrairu 25, 2021
Masu Fataucin Abinci Da Dabbobi Sun Shiga Yajin Aiki A Najeriya
Facebook Forum