Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Najeriya Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jirage a Abuja, Legas


Filin jirgin sama na kasa da kasa a Abuja, Najeriya
Filin jirgin sama na kasa da kasa a Abuja, Najeriya

Hukumar da ke kula da zirga-zirgar jiragen sama a Najeriya NCAA, ta ce za ta dakatar da zirga-zirgar jiragen sama na kasa da kasa a Abuja da Legas.

NCAA ta bayyana hakan ne a ranar Asabar a wani mataki na dakile yaduwar cutar coronavirus da ke bazuwa a duniya kamar yadda gidan talbijin na Channels ya ruwaito.

Wannan sabon mataki zai fara aiki ne a ranar Litinin 23 ga watan Maris, zai kuma kai har nan da wata guda a cewar wata sanarwa da NCAA ta fitar.

Jaridar Daily Trust wacce ita ma ta tabbatar da labarin, ta bayyana cewa, jiragen da ke jigila a cikin gida za su ci gaba aiki.

A dai ranar Juma’a hukumar ta NCAA ta ayyana dakatar da jigilar jiragen kasa da kasa a filayen jirgin sama na Malam Aminu Kano da ke Kano, Akanu Ibiam da ke Enugu da kuma na Fatakwal da ke jihar Rivers.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG