Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ministan Harkokin Wajen Iran Yace Akwai Rashin Fahimta Kan Batun Jigilar Makamai Zuwa Najeriya


A car drives past the Iranian Embassy in Abuja, Nigeria, Friday, Nov. 12, 2010. Nigeria will take actions against Iran if an investigation shows it violated international law and U.N. sanctions in an arms smuggling case, Nigeria's foreign minister said Fr
A car drives past the Iranian Embassy in Abuja, Nigeria, Friday, Nov. 12, 2010. Nigeria will take actions against Iran if an investigation shows it violated international law and U.N. sanctions in an arms smuggling case, Nigeria's foreign minister said Fr

Litinin din nan ce aka ji Manoucher Mottaki yana gayawa Majalisar Dinkin Duniya cewa akawai rashin fahimta a zargin d a ake yi wa Iran gameda jiglar makamai ta hanun 'yan kasuwa zuwa Najeriya.

A yau litinin aka ji Ministan harkokin wajen kasar Iran Manoucher Mottaki yana shaidawa Majalisar Dinkin Duniya cewa akwai rashin fahimta a zargin da ake yiwa Iran da laifin jigilar makamai ta hannun ‘yan kasuwa zuwa Nigeria inda jami’an tsaro suka chafke su bayan bincike.

Yace yanzu matsalar da hakan ta haifar an kauda ita. Idan an tuna Juma’ar data gabata ce hukumomin Nigeria suka yi barazanar kai karar Iran gaban kwamatin sulhun Majalisar Dinkin Duniya saboda keta haddin takunkumin da Majalisar ta aza mata.

A wani labarin kuma, Wani kamfanin ayyukan binciken mai na Amurka ya bada sanarwar samun nasarar gano rijoyoyin man fetur a gabar tekun kasar Saliyo.Shi wannan kamfanin mai mai suna Anadarko da cibiyarsa ke Texas Amurka ya bada sanarwa gano rijiyar danyen mai- lakabin “Mercury-1” a karkashin ruwan teku da tazarar kilomita hamsin daga bakin gabar ruwan tekun Saliyo.

Kamfanin yace zai kokarta yin aikin hadin gwiwa tare da wani kamfanin da kuma hannun Gwamnatin kasar Saliyo.

XS
SM
MD
LG