Shugaba Muhammadu Isuhu na Nijar, ya nada shugaban jam'iyyar MNSD Nasara a zaman wakilin shugaban kasa. Wannan nadin, yasa masu sharhi suna ganin kamar ba zai rasa nasaba da amsa gayyatar da shugaban na Nijar ya yiwa 'yan hamayya cewa, su taho a kafa gwamnatin hada kan kasa ba.
Yanzu nadin ya janyo muhawara ta ko ina a fadin kasar musamman a dandalin sada zumunta.
Wasu 'yan kasar da suka tofa albarkacin bakinsu kan wannan batu, sunce sam- sam wannan mataki ba shine zai warware dumbin bukatun al'umar kasa ba, wadanda suka hada da kuncin rayuwa da dai sauransu.
Ga karin bayani.