Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Palestinu Tayi Barazanar Yanke Hanyoyin Sadarwanta Da Amurka


Bosnia-Herzegovina- Protest to support people of Palestine, Sarajevo, 23Nov2012.
Bosnia-Herzegovina- Protest to support people of Palestine, Sarajevo, 23Nov2012.

Palesdinu ta bukaci Amurka data yi watsi da kiran da Izreala ke mata game yunkurin wargaza samar da zaman lafiya tsakanin kasashen biyu.

2

US PALESTINIAN, 11/19/17 1500

CN: 20951331, TRANSLATOR: LADAN

Gwamnatin Palesdinu tayi barazanar yanke dukkan wasu hanyoyin sadarwa tsakanin ta da Amurka muddin gwamnatin shugaba Donald Trump taci gaba tayi anfani da yunkurin ta na kulle mata ofisoshin jakadancin ta dake nan Washington DC.

A cikin wani vidieo ta hanyar sadarwan zamani an nuna daya daga cikin manyan jamian Palesdinun Saeb Erakat wanda shine ke shiga tsakani akan wannan batu yana sukan lamirin gwamnatin Amurka yana cewa tana neman ta bada kai bori ya hau domin gwamnatin Israela ta matsa mata lamba, Yace wannan na faruwa ne ko domin kungiyar neman ‘yancin Palesdinu na matsa kaimi ga babban kotun duniya ta kasa-da-kasa cewa kotun ta tabbata taga cewa an hukunta Israelawa dake cutar da Palesdinawa.

Saeb yaci gaba da cewa ba zasu yarda da wannan yunkurin ba, yace gwamnatin Netenyahu ce ke kokarin ganin sukurkuta yunkurin samar da zaman lafiya a tsakanin kasashen biyu, Yace domin cimma wannan buri nasu yasa gwamnatin ta Israela ke kokararin lalata kome a halin yanzu, alhali batun samar da zaman lafiya yayi nisa tsakanin su.

Sai dai kawo yanzu gwamnatin Amurka bat ace kome ba game da wannan batu ba, amma ofishin Netenyahu yace kulle ofishin da Amurka tace zata yi shawara ce da ya rataya kan Amurka dama dokokin ta.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG