Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Pence: Ana Samun Ci Gaba A Tattaunawarmu Da Mexico


A yau Juma’a ne Jami’ai daga Amurka da Mexico suke komawa kan teburin tattaunawa, don neman hanyar da za’a magance matsalar kwararowar baki haure daga kasashen nahiyar Amurka ta tsakiya, zuwa kan iyakar kudancin Amurka da ya janyo barazanar cinikayya tsakanin kasashen makobtan juna.

A jiya Alhamis Amurka ta matsawa Mexico don ta kara kokarin hana karuwar bakin haure daga nahiyar Amurka, da suke tunkaro arewaci don zuwa Amurka.

Yayin da shugaba Donald Trump, ya sake sabunta barazanar sa ta saka harajin kashi biyar cikin dari akan dukkan kayayyakin dake shigowa daga Mexico a sati mai zuwa idan dai ba’a cimma wata yarjejeniya ba.

Mataimakin shugaban kasar Amurka, Mike Pence, yace ana samun ci gaba a zantawar da suke da Mexico a wannan satin.

Sai dai amma ya kuma ce Amurka tana so kasar Mexico ta kara kokari, don hana kwararowar dubban bakin haure dake fitowa daga kasashen Guatemala, Honduras, da kuma El Salvador.

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG