Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Peter Obi Ya Zabi  Datti-Baba Ahmed A Matsayin Dan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa A Jam'iyyar LP


Datti Baba-Ahmed, hagu, da Peter Obi, dama (Hoto: Facebook/Peter Obi Movement)
Datti Baba-Ahmed, hagu, da Peter Obi, dama (Hoto: Facebook/Peter Obi Movement)

Obi ya kuma nuna kwarin gwiwar cewa Baba-Ahmed zai yi amfani da dumbin iliminsa wajen ganin an cin ma burin da suka sa a gaba na ‘Rescue Nigeria Project’ – wato shirin kubutar da Najeriya don a kyautata makomarta.

Rahotanni daga Najeriya na nuni da cewa , dan takararar shugaban kasa karkashin jam’iyyar Labour Party a Najeriya, Peter Obi, ya bayyana sunan wanda zai masa takarar mataimakin shugaban kasa a zaben 2023.

Obi ya bayyana Datti Baba-Ahmed a matsayin abokin takararsa a ranar Juma’a a Abuja, babban birnin Najeriya.

Yayin sanar da sunan Baba-Ahmed, Obi ya ce, lokaci ya yi da za a kubutar da Najeriya don ta zama kasa abin koyi.

“An sha yi a kasashe masu tasowa da dama, ba wani abu ba ne mai sarkakiya.

“Mu matasa ne, masu jini a jika, za kuma mu dukufa wajen ganin mun mayar da makeken yankin arewa tushen hanyar samun man fetur a nan gaba. In ji Obi.

Ya kara da cewa, jihar Kano da Kaduna, za su zama cibiyoyin sarrafa kayayyaki a Najeriya.

Obi ya kuma nuna kwarin gwiwar cewa Baba-Ahmed zai yi amfani da dumbin iliminsa wajen ganin an cin ma burin da suka sa a gaba na ‘Rescue Nigeria Project’ – wato shirin kubutar da Najeriya don a kyautata makomarta.

Baba-Ahmed, wanda shekarunsa ba su kai hamsin ba, shi ne mamallakin jami’ar Baze University da ke Abuja da kuma jami’ar Baba-Ahmed da ke Kano.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG