Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Qatar 2022: Ronaldo Zai Fara Tallata Kansa A Gasar Cin Kofin Duniya


Cristiano Ronaldo
Cristiano Ronaldo

Wannan shi ne karo na biyar da Ronaldo yake zuwa gasar cin kofin duniya, ta kuma yi wu, shi ne karo na karshe.

Ga dukkan alamu, dan wasan Portugal Cristiano Ronaldo, zai yi amfani da gasar cin kofin duniya da ke wakana a Qatar wajen tallata kansa ga kungiyoyin da ke sha’awar sayensa.

A ranar Talata Manchester United ta raba gari da Ronaldo, bayan wata zazzafar hira da ya yi, inda ya caccaki kocin kungiyar ta United da shugabanninta.

Dan shekara 37, Ronaldo, wanda yanzu haka ba shi da kungiya, zai jagoranci tawagar Portugal wajen karawa a wasansu na farko da Ghana.

Wannan shi ne karo na biyar da Ronaldo yake zuwa gasar cin kofin duniya, ta kuma yi wu, shi ne karo na karshe.

Wasan na Portugal da Ghana zai wakana ne a filin wasa na Stadium 974 a Doha, babban birnin Qatar a ranar Alhamis.

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG