Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Qatar Ta Bukaci Kuwait Ta Shiga Tsakanin Domin Sasanci


Kasar Qatar tace tana son ganin Kuwait ta zama mai shiga tsakani ta tuntubi sauran kasashen da zummar kashe wutar rikicin.

Ministan harkokin wajen Qatar Sheiekh Mohammed bin Abdulrahman al-Thani, yayi kiran da a samu masu shiga tsakani domin warware rikicin difilopmasiyya, da ya sa kasashen Saudiyya da wasu kasashen larabawa biyar suka tsinka huldar jakladanci da hukumomin kasar dake Doha.

Kasashen Masar da Yemel, da hadaddiyar daular larabawa, da Bahrain, da Maldives suna zargin kasar Qatar da goyon bayan mayakan sakai masu ikirarin islama da kuma kasar Iran.

Qatar ta kira zargin maras tushe wanda bashi da wata madogara.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG