Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Rikicin Taraba Ya Raba Mutane Dubu Uku Da Muhallansu


Gwamnan Taraba dake kan jinya har yanzu
Gwamnan Taraba dake kan jinya har yanzu

Ban da mutanen da suka rasa rayukansu da wadanda suka jikata da wadanda suka bace wasu iyalai dubu uku sun rasa muhallansu.

Yayin da ake bi daji daji domin a gano wadanda suka bace banda wadanda suka mutu ko suka jikata, rikicin da ya samo asali a kauyen karamar hukumar Ibi a jihar Taraba ya raba iyalai dubu uku da muhallansu.

Mutanen da suka rasa gidajensu sanadiyar hare-hare da mutanen Tarok suka kai masu suna cikin wani halin lahaula walakawati. An kone gidanjensu kana su da yaransu suna nan kara zube a wasu makarantu firamari inda ba wuta ba ruwa sai sauro da suka dira kansu.

Hukumomin Taraba sun tabbatar da cewa muatane fiye da dubu uku suke gudun hijira banda wadanda suka bace domin ba'a san inda suke ba. Sun ce gwamnati na iyakacin kokarinta ta taimaki mutanen.

Ibrahim Abdulaziz nada rahoto.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:27 0:00
Shiga Kai Tsaye
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG