WASHINGTON, D.C —
Yaduwar cutar coronavirus wadda ake alakantawa da wani wurin shakatawa na dare a birnin Seoul na kasar Koriya Ta Kudu, ya janyo tsana ga ‘yan luwadi.
Hakan na faruwa ne bayan da aka alakanta barkewar annobar da ‘yan luwadi masu zuwa wurin.
A yayin da Koriya Ta Kudu ta yi nasara wajen takaita yaduwar cutar corona cikin ‘yan makonnin nan, dada yaduwa da sabuwar bullar coronar ke yi, wadda ake alakantawa da wuraren shaye-shaye da shakatawa a birnin na Seol, ya janyo farbagar yiwuwar barkewar cutar a karo na biyu, da kuma kyamar ‘yan luwadi.
Daga cikin sabbin kamuwar, guda 29 ne aka tabbatar suna da nasaba da wani wurin shakatawar dare mai suna Itaewon, wanda ‘yan luwadi suka fi zuwa.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 18, 2021
Kungiyar Kasuwanci ta Duniya Na Bukatar Sabon Salon Gudanarwa-Dr. Ngozi
-
Fabrairu 18, 2021
Guterres Ya Yi Kiran a Samar Da Tsarin Bai Daya Na Rigakafin Coronavirus
-
Fabrairu 16, 2021
Kungiyar WTO Ta Gabatar Da Sabuwar Shugaba Ngozi Okonjo-Iweala
-
Fabrairu 16, 2021
Hukumar Lafiya Ta Duniya (WHO) Ta Aminta Da Riga Kafin AstraZeneca
Facebook Forum