Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sanata Joshua Lidani Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Jihar Gombe


Wasu matasan Gombe da aka horas
Wasu matasan Gombe da aka horas

Matasan kudancin jihar Gombe sun fusata da Joshua Lidani dan majalisae dattawa dake wailtarsu bisa yin watsi dasu tun lokacin da aka zabeshi

Wasu matasa sun hana Sanata Joshua Lidani fita daga fadar sarkin Waja a garin Talasi yayinda ya kai gaisuwar bangirma ga basaraken.

Malam Isa Kwani wanda lamarin ya faru a gabansa ya yiwa Muryar Amurka karin haske game da abun da ya faru a fadar sarkin har ta kaiga harbin wani matashi a kafa..

Inji Mala Isa Sanata din ya je hedkwatar karamar hukumar Balanga ne duba aikin da ake yiwa mazabarsa sai ya je fadar saki gaisuwa. Da ya shiga fadar matasan suka ce ba zai bar fadar ba saboda wai tunda aka zabeshi bai je garin ya yi godiya ba. Bai taba zuwa ya ji koke-koken jama'arsa ba ko ya san damuwarsu. Dalili ke nan da matasan suka fusata suka kai masa hari.

Sojoji da aka tura daga Gombe suka ceto shi Sanata Lidani bayan sun harbi wani matashi daya a kafa.

Amma a cewar shi Sanata Lidani ya danganta abun da ya faru dashi akan jam'iyyar adawa ta APC inda ya kara da cewa matsalolin matasa a Najeriya ruwan dare gama gari ne.

Ga rahoton Abdulwahab Muhammad da karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:04:06 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG