Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kasar Saudiyya Ta Kama Mutane Fiyeda 400 kan Zargin Alaka Da KUngiyar ISIS.


Nutane suke kallo bayan harin da wani dan kunar bakin wake ya kai kan masallacin 'yanshi'a a wani yanki na Saudiyya, a cikin watan Mayun bana.
Nutane suke kallo bayan harin da wani dan kunar bakin wake ya kai kan masallacin 'yanshi'a a wani yanki na Saudiyya, a cikin watan Mayun bana.

Ma'aikatar harkokin cikin gidan kasar ce ta bada sanarwar haka ranar Asabar.

Kasar Saudiyya ta kama fiyeda mutane 400, galibinsu 'yan kasar kan zarghin suna da alaka da kungiyar ISIS.

A cikin sanarwar da ma'aikatar harkokin cikin gidan kasar ta fitar da kamfanin dillancin labarai na kasar ta wallafa, tace kama mutanen wani banagare ne na gagarumin matakin tsaro da kasar ta dauka domin dakile wani shirin kai hare hare da kungiyar ISIS ta shiya zata kai kan masallatai, da wani ofishin jakadanci, da ofisoshin jami'an tsaro, dana gwamnati a lardin Sharurah na kasar.

Wannan sanarwa tana zuwa ne kwana daya bayan kungiyar ta ISIS ta kai hari kan waa kasuwa cike makil da jama'a a lardin Diyala a Iraqi ta kashe mutane 115.

XS
SM
MD
LG