Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shaye Shaye Ne Ke Haddasa Juyewar Kwakwalwa Ga Matasa


Fasta na 'yan takara a Yamai, babban birnin Nijar
Fasta na 'yan takara a Yamai, babban birnin Nijar

Ranar 10 ga watan Oktobar kowacce shekara rana ce da Majalisar Dinkin Duniya ta ware domin tunawa da mutane masu tabin halkali a fadin Duniya.

Wakiliyar Muryar Amurka a Jamhuriyar Nijar Tamar Abari, ta ziyarci sashen da ake kula da masu tabin hankali na babban asibitin Damagaram, mafi yawan marasa lafiyar matasa ne kuma shaye shayen kayen maye ne ya haddasa musu juyewar kwakwalwa, a cewar Lawali Girema jami’in dake kula da masu tabin hankali a asibitin.

A cewar Lawali, tabin hankli na wannan zamani mafi yawancin mutanen da ke fama da shi samari ne masu yin shaye shaye, sai kuma wanda ake samu sanadiyar Aljanu da kuma ciwon dake samun mata bayan haihuwa wanda ke taba kwakwalwarsu.

Babban abin yi anan shine hukumomi su kara kaimi wajen yaki da safarar miyagun kwayoyin dake zama ummul aba’isin wannan matsala ga matasa.

Saurari cikakken rahotan Tamar Abari.

please wait

No media source currently available

0:00 0:04:03 0:00

XS
SM
MD
LG