Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaba Buhari Da Majalisar Dokokin Kasa Na Cigaba Da Jayayya Kan Jadawalin Zabe


Shugaba Muhammadu Buhari
Shugaba Muhammadu Buhari

Da alamar za a shiga wata sabuwar rigima tsakanin Fadar Shugaban Najeriya da Majalisar Dokokin kasar saboda yinkurin canza jadawalin zabe da Majalisar ke yi, a yayin da shi kuma Shugaba Buhari ke son a bar shi yadda ya ke.

A cigaba da ja-in-jar da ake yi tsakanin Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da Majalisar Dokokin kasar kan batun sabunta jadawalin zabe, bayan da Shugaba Buhari ya bayyana ma Majalisar dalilansa na kin sanya hannu kan kudurin dokar sauya jadawalin zaben, wasu ‘yan Majalisar sun mai da martani.

Tuni dai aka shiga muhawara kan wannan batu a fadin kasar. Kudurin dokar gyarar dokar zaben, ya nuna cewa za a soma zaben ne da na Majalisar Dokokin Tarayya kuma na Shugaban kasa ne zai zo karshe. Wannan ya saba ma yadda ya ke a yanzu, wato yadda Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta tanadar a kundin zaben da ta bayyana a watan Nuwamban bara.

Sanata Shehu Sani dan jam’iyyar APC, ya ce yanzu ya rage ga Majalisar ta kada kuri’a tsakanin masu goyon bayan matsayin Shugaba Buhari da kuma masu ra’ayin Majalisar Dokokin kasar. Ya ce duk bangaren da ya yi rinjaye ra’ayinsa ne zai tabbata. Shi kuwa wani dan Majlisar wakilai mai suna Ahmed Babba Kaita ya ce matakin da Shugaba Buhari ya dauka ya yi daidai:

Ga Madina Dauda da cikakken rahoton:

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:48 0:00

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG