Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan wanda yake ziyara a kasar Sin ya samu ganawa da Shugaban kasar Xi Jinping inda ake zato zai zartar da shirya samun lamuni na biliyoyin daloli a kan kudin ruwa kalilan domin gudanar da ayyukan gine-gine a Najeriya kamar su hanyoyi, gina madatsun ruwa domin samarda wutar lantarki da cigaba da aikin hakar mai da iskar gas.