Shugaban Amurka Donald Trump, ya ce, takwaran aikinsa na Korea ta Arewa, Kim Jong Un, ya “dan ba da hakuri” saboda gwajin makamai masu linzami da kasarsa ta yi.
Ya kuma kara da cewa, Shugaba Kim, ya sha alwashin, zai dakatar da gwaje-gwajen, da zaran Amurka da Korea ta Kudu ,sun kammala atisayen hadin gwiwar da suke yi.
Shugaban na Amurka ya ce, Kim ya ba da hakurin ne, a wata wasika da ya aiko masa, ya kuma ce, yana da burin “su hadu su tattauna” bayan an kammala atisayen.
A ranar Litinin din da ta gabata, Amurka da Korea ta Kudu suka fara atisayen, wanda ake shirin kammala shi a ranar 20 ga watan nan na Agusta.
Za ku iya son wannan ma
-
Afrilu 09, 2021
Mawakin Gambara DMX Ya Mutu
-
Afrilu 09, 2021
Dan Najeriya Da Ya Zama Kyaftin Din Jirgin Yakin Ruwan Amurka
-
Afrilu 03, 2021
An Kashe Wani Dan Sandan Ginin Majalisar Dokokin Amurka
-
Maris 31, 2021
Kakar Barack Obama Ta Rasu