Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaba Kim Ya Gargadi Amurka Kan Takunkumanta


Trump Kim Summit

A wannan makon ne shugaba Trump ya ce, yana duba yiwuwar sake wani zama da Kim, amma ya jaddada cewa, Amurka ba za ta sassauta takunkumin da ta sakawa Korea ta Arewan ba, har sai ta lalata makamanta na nukiliya.

Shugaban Korea ta Arewa Kim Jong Un, ya ce zai bai wa Amurka wa’adin nan da zuwa karshen shekarar nan, domin ta dauki kwakkwarar matsaya kan tattaunawar da suke yi game da batun nukiliyanta.

Kim ya yi gargadin cewa, za a iya fuskantar mummunan sakamako, muddin hukumomi a Washington, ba su sauya yadda suke tafiyar da wannan al’amari ba.

Yayin da yake jawabi a gaban majalisar dokokin kasar, wacce ake mata kallon ta jeka-na-yi-ka ce, shugaba Kim, ya ce a shirye yake ya kara wata tattaunawa ta uku da takwaran aikinsa Donald Trump, amma har sai Amurka ta sauya irin halayarr da take nunawa, kamar yadda kafar yada labaran kasar ta Korea ta Arewa ta bayyana.

A wannan makon ne shugaba Trump ya ce, yana duba yiwuwar sake wani zama da Kim, amma ya jaddada cewa, Amurka ba za ta sassauta takunkumin da ta sakawa Korea ta Arewan ba, har sai ta lalata makamanta na nukiliya.

“Muna so takunkuman su ci gaba da kasancewa, a irin tawa fahimtar, ba mu nuna matsi sosai ba.”

Facebook Forum

An Sami Karuwar Farashin Kayayyaki A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:42 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Shiye-Shiryen Shiga Watan Azumi A Kasar Ghana
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:56 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Ziyarar Sakatare Blinken A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Al'umomi Sun Koka Game Da Tashin Farashin Kayayyaki
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG