Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaban Amurka Zai Karbi Bakoncin Shuwagabannin Afirka


Shugaban Amurka Barack Obama
Shugaban Amurka Barack Obama

Shugaban Amurka Barack Obama zai karbi bakuncin shugabannin Afirka a wani taro na kokarin inganta huldar cinakayya da saka jari da nahiyar.

Fadar White House ta bayar da sanarwar shirin taron a jiya Talata, da cewa za a yi ne a ranakun 5 da 6 ga watan Augusta a nan birnin Washington.


Baya ga batun cinakayya, a cewar Fadar ta White House, Mr. Obama zai yi amfani da damar wajen jaddada alwashin da Amurka ta sha na tabbatar da tsaro da inganta demokaradiyya a Afirka.

Nan take dai ba a bayyana shugabannin Afirkan da za a gayyata taron ba.
XS
SM
MD
LG