Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaban Tanzania


Al’ummar Tanzania sun fara shakku gameda isasshiyar lafiyar shugabansu, bayanda ya sake faduwa, ya some a gaban bainar jama’a.

Mutanen Tanzania na can suna ta nuna damuwa da yi wa juna tambayoyi gameda halin lafiyar shugaban kasar tasu, Jakaya Kikwete, wanda ya fadi, ya some a lokacinda yake kaddamarda bikin soma kyamfen dinsa na neman zabe a ranar Assabar da ta gudana. Rahottani sunce shugaba Kikwete ya yanke, ya fadi ne a lokacinda yake cikin yiwa dubban magoya bayansa jawabi a birnin Dar-es-Salam. Sai dai wasu sunyi sauri sun cafke shi kafin ya fadi kasa, kuma bayan ya fita, bai dade ba, ya dawo, yace ala-tilas sai da ya karya azuminsa. Wannan dai shine karo na ukku da shugaba Kikwete, dan shekaru 59 da haihuwa, yake taba faduwa, yana somewa a bainar jama’a. A shekarar 2005 an taba irin wannan, a lokacinda shugaban ya fadi a cikin wannan filin wasan da abin ya faru a wannan karon. Sannan kuma ya sake maimaita irin hakan a watan Oktoban da ya gabata. Shine yanzu al’ummar Tanzania ke neman shugaban ya gaya musu gaskiya idan yana fama da wata matsala ta rashin lafiya.

XS
SM
MD
LG