Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaban Turkiya Edorgan Ya Lashe Zaben Shugaban Kasarsa


Shugaban Turkiya Recep Tayyip Edorgan da matarsa

Nasarar da Shugaban Turkiya Recep Tayyib Edorgan ya samu a zaben da aka yi jita ta bashin wa'adin mulki na shekara biyar tare da kara masa ikon mulki da karfin ikon fada a ji

Shugaban Turkiyya, Recep Tayyib Erdogan, ya lashe zaben shugaban kasar da aka yi, nasarar da ta ba shi wani sabon wa’adi, yayin da ofishin shugaban kasa ke ci gaba da samun karin karfin ikon fada a-ji.

Kafar yada labaran gwamnati ta ce, Erdogan ya lashe kashi 53 cikin kashi 100 na kuri’un da aka kada a zaben da aka yi a jiya Lahadi.

Shi kuma Muharrem Ince, na jam’iyyar adawa ta Republican People’s Party (CHP), ya samu kashi 31 cikin 100.

Wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a a aka jefa a shekarar 2017, ta haifar da sauyi a tsarin siyasar kasar, wanda ya soke ofishin Firai Minista, ya kuma karawa na shugaban kasa karfin ikon sallamar majalisar dokoki, ya kuma nada minisitoci da alkalai.

A wani jawabi da ya yi, shugaba Erdogan ya ce, “alumar kasarsa sun mika mai amanar shugabantar kasar tare da gudanar da ayyuka.”

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG