Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaban Zimbabwe Robert Mugabe Ya Kori Mataimakinsa daga Mukaminsa


Mataimakin Shugaban Kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa da Shugaban kasar Robert Mugabe ya tsige
Mataimakin Shugaban Kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa da Shugaban kasar Robert Mugabe ya tsige

Korar mataimakin shguaban kasar Emmerson Mnangagwa, kila ya budewa matar Mugabe, Grace, kofar zama shugabar kasa, wadda ta fito ta nuna sha’awar haka shekaru uku da suka gabata.

A can kasar Zimbabwe kuwa, shugaban kasar, Robert Mugabe ne, ya kori mataimakinsa, wanda aka taba zatonshi zai gaje shi.

A jiya Litinin ne gwamnatin kasar ta sanar da cewa, an cire Mnangagwa daga mukaminsa, kuma korar ta fara aiki nan take.

Bayanin korar ya zo ne daga ministan yada labarai Simon Khaya Moyo, wanda ya fadawa sashen Zimbabwe na Muryar Amurka cewa “mataimakin shugaban kasar ya kasance mai nuna halayen rashin biyaya da girmama na gaba da yaudara da kuma rashn sanin ya kamata ko kuma nuna datako.

Am dade ana gani alamun korar Mnangagwa daga mukaminsa, amma sai karshen makon da ya gabata ne, lokacin wani gangamin matasan jam’iyya mai mulki a birnin Bulawayo, al’amarin ya rincabe.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG