Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugabanin Mata a Yankin Arewa na Ganin Yakamata 'Yan Arewa su Farga


'Yan gudun hijira sandiyar hare-haren 'yan Boko Haram sun karban kayayyakin agaji da suka hada da abinci a sansanin 'yan gudun hijira a Yola.
'Yan gudun hijira sandiyar hare-haren 'yan Boko Haram sun karban kayayyakin agaji da suka hada da abinci a sansanin 'yan gudun hijira a Yola.

Akwai alamun ana amfani da wasu 'yan siyasan Arewa don cinma wani buri dan gane da rikicin boko haram

Wasu shugabannin mata a Arewacin Najeriya na ganin cewar a na amfani da ‘yan siyasan Arewa don cimma wani buri, ganin yadda dubban mata da yara ke cikin halin ha’ula'i a yankin Arewa maso gabasa sanadiyyar rikice-rikicen kungiyar boko haram.

A cewar Hajia Hadiza Ningi, wada ake ma lakani da Hadiza ‘yar Ganye, tana ganin ba da gaske ake ba don ganin a kawo karshen wannan matsalolin na rashin tsaro a kasar baki daya ba. Tace a duk Najeriya babu yankin da ke da manya da yakai yankin arewa, amma ‘yayan su da jikoki da ake kashewa baji bagani, su gaskia basu ga alamar ana neman magance matsalara ba, don su mahukuntar suna babban birnin tarayya Abuja suna kwasar kudi.

Ta kara da cewar, ai Dr. Bawa Wase yace muna da karfin sojoji da zasu yaki kungiyar boko haram, amma anki daukan matakai da suka kamata. Alkalunmma na nuni da cewar mata da yara kanana su sukafi yawa a sannsanin ‘yan gudun hijira. Wannan batun na neman kulawa ta musamman a cewar Alh. Sa’adu Bello, jami’in hukumar bada agajin gaggawa ta NEMA da ke kula da sannsanonin ‘yan gudun hijira a jihar ta Adamawa, yayi kira da gwamnatocin jihohin Arewa da ko ina a kasar, da su bada gudun mawa ga ‘yan gudun hijira da ke kwarara zuwa jihohinsu.

Shima babban jami’in hukumar Red Cross me kula da jihohin Arewa maso gabas, Alh. Aliyu Mekano, yayi Karin haske ga irin taimako da suke badawa, yace wannan ba wai taimako ne kawai na bangare dayaba, wannan yashafi kowa musamman ma ‘yan siyasa yakamata su bada tasu gudun mawa don taimakama wadanda ke neman taimakon gaggawa.

Shugabanin Mata a Yankin Arewa na Ganin Yakamata 'Yan Arewa su Farga - 2'48"
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:48 0:00
Shiga Kai Tsaye

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG