Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugabannin Afirka Su Na Yin taron Koli A Kasar Equatorial Guinea


Tutocin kasashen Afirka a babban filin jirgin saman Malabo a kasar Equatorial Guinea, inda aka fara gudanar da taron koli na 17 na Kungiyar Tarayyar Kasashen Afirka
Tutocin kasashen Afirka a babban filin jirgin saman Malabo a kasar Equatorial Guinea, inda aka fara gudanar da taron koli na 17 na Kungiyar Tarayyar Kasashen Afirka

Batun rikicin kasar Libya da yadda za a shawo kan sa shi ne zai mamaye wannan taron kolin kwanaki biyu na Kungiyar Tarayyar Kasashen Afirka

Shugabannin Afirka sun bude taron kolin da ake sa ran zai fi mayar da hankali kan rikicin da ake yi a kasar Libya. Ana wannan taron kolin ne a kasar Equatorial Guinea.

Wani kwamiti na shugabannin kasashen Afirka biyar yana kokarin tsara wani shirin kawo karshen rikicin, wanda kuma za a gabatar a gaban taron kolin domin neman amincewarsa. Shirin ya kunshi kiran da a tsagaita wuta a Libya tare da shirya zabe na dimokuradiyya.

Su kuma ‘yan tawayen Libya su na son shirin ya kunshi kiran da shugaba Muammar Gaddafi na Libya yayi murabus nan take. Wakilan ‘yan tawaye da na gwamnatin shugaba Gaddafi su na halartar wannan taron kolin kwanaki biyu.

Haka kuma, shugabannin na Afirka zasu tattauna halin da ake ciki a kasar Sudan. An shirya Kudancin Sudan zata zamo ‘yantacciyar kasa a ranar 9 ga watan Yuli, amma kuma sassan su na gwabza fada a wasu sassan na bakin iyakarsu.

XS
SM
MD
LG