A lokacinda suka bayyana jiya a gaban Kwamitin Harakokin Soja na Majalisar Dattawan Amurka, shugaban Hukumar Leken Assirai, James Clapper da shugaban Hukumar Tsaro Michael Rogers da kuma karamin sakataren ma’aikatar tsaron Amurka na Amurka Marcel Lettre, sun ce ra’ayinsu yazo daya akan cewa abinda suka kira “shugabannin kul da kul” na Rasha ne kawai ke da ikon bada iznin a yi irin wannan shisshigi da satar bayanai na asirin wata kasa.
Sun kuma bayyana abinda Rasha din tayi da cewa “barazana ce ga muradun” Amurka.
Sai dai kuma Clapper yace ba zasu iya auna tasirin aibin da bayanan da cibiyar Wikileakes ta sako akan zaben ba.
Shugaban Amurka mai bari gado Barack Obama ne ya umurci hukumomin leken assiran su bi diddigin duk shisshigin da ake jin wasu kasashen ketare sunyi a harakokin zabe, tun daga zaben da aka yi a shekarar 2008 har zuwa yau.