Wasu sojoji cikin motar a kori kura a cikin birnin Bauchi sun budewa motar da ake tuka Professor Ango Abdullahi wuta
A hira da sashen Hausa Professor Ango Andullahi yayi bayanin cewa suna kan hanyarsu ta zuwa Gadau a Azare suna kan hanyarsu a cikin garin Bauchi, Sai suke iske wata motar soja a kori kura a gabansu. A lokacinda direbansa yayi kokarin wuce motar sojan, sai sojoji suka yi ta harbi motar su, al'amarin daya sa ramin harsashe har goma sha daya a jikin motar.
Professor Ango Abdullahi yace, dama an dade suna zargin cewa ana kashe mutane kamar kiyashi. Kuma wannan al'amari ya faru ne ba' a wurin da ake duba motoci bane, balle ace direbansa yaki tsayawa.
Cikin ikon Allah dukkansu mutane hudu dake cikin motar Professor Ango Abdullahi babu wanda yaji rauni. Yace shugaban sojoji yaje wurin ya bashi hakuri, ya kuma ce za'a gudanar da binciken dalilin daya sa sojoji suka budewa motarsa wuta.