Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sojojin Najeriya Na Ci Gaba Da Sintiri A Sambisa


Yanzu dai kusan mako daya kennan da kwato dajin Sambisa, daga hannun mayakan Boko Haram,. Rahotani na tabbastar da cewar dakarun Najeriya na ci gaba da yin sintiri a koina cikin wannan dajin.

Daraktan labarai na dakarun Sojojin Najeriya, Brigediya janar Sani Usman Kuka Sheka, yace a yanzu ‘yan ta’adda na Boko Haram, basuda wani sansani a cikin dajin Sambisa, wanda suke iko dashi.

Ya kara da cewa basu da sauran wata laka da zasu iya kai wani hari a kungiyance, yana mai cewa Sojojin Najeriya, zasu yi kokari duk inda ‘yan kungiyar ta Boko Haram, suke a tabbatar da anyi maganinsu.

A nashi bangare tsohon Gwamnan jihar Yobe Sanata Abba Ibrahim, wanda a zamanin mulkinsa yayi fama da ‘yan Taliban din Najeriya, wadanda daga baya suka zama ‘yan Boko Haram, yace kwato dajin Sambisa, babban nasara ne da ci gaba a Najeriya.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:35 0:00

XS
SM
MD
LG