Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sojojin Najeriya Na Shirin Kai Farmaki Katsina


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ba da umurnin a kaddamar da wani farmakin soji na musamman domin magance matsalar ‘yan ta’adda da masu garkuwa da mutane a jihar Katsina.

Wata sanarwa da mai taimakawa Buhari a fannin yada labarai Garba Shehu ya fitar Lahadi, ta nuna cewa “dakarun kasar na musamman sun fara wani shiri, wanda har yanzu ba a yi cikakken bayani a kansa ba.”

Shirin a cewar sanarwar, “zai dakile hare-haren da ake kai wa a sansanonin ‘yan gudun hijira.”

Domin kaddamar da wannan shiri, wata tawaga ta musamman ta isa jihar don tsara yadda za a aiwatar da wannan farmakin da “ba a taba ganin irinsa ba.”

Tuni dai babban hafsan soji mai kula da harkokin tsaro, Janar Olonisakin, ya yi wa shugaba Buhari bayani kan yadda yake sa ran za a gudanar da wannan shirin a cewar Shehu.

Shugaba Buhari wanda ya nuna baccin rai kan yawan hare-haren da ake kai wa a jihar, ya kuma jajantawa iyalan wadanda suka rasu sanadiyyar hare-haren.

A ‘yan kwannakin nan, jihar ta Katsina na fuskantar karin hare-hare wadanda kan jawo asarar rayuka da dama.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG