Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sojojin Najeriya Sun Dawo Gida


Manjo-janar Chris Olukolade da Rear Admiral E.O. Ogbor su na jawabi ga masu zanga-zanga yau talata a hedkwatar rundunar sojojin Najeriya a Abuja.
Manjo-janar Chris Olukolade da Rear Admiral E.O. Ogbor su na jawabi ga masu zanga-zanga yau talata a hedkwatar rundunar sojojin Najeriya a Abuja.

Manene hukumcin da sojojin zasu fuskanta

Sojojin Najeriya, dasuka haura kasar Kamaru, sun dawo gida Najeriya, kwanaki uku bayan arcewarsu zuwa kasar ta Kamaru.

Kamar yanda rahotanin ke cewa Sojojin, sun komo ne ta yankin, mubi dake kan iyakan Najeriya, da kamaru, a arewacin jihar Adamawa, a cikin wani yanayi na ban tausayi.

Masanin harkar tsaro, majo Yahaya Chiku, mai ritaya na ganin cewa akwai abun dubawa kamai da wannan batu da kuma matakin da rudunar Sojojin Najeriya, tace zata dauka kan wadannan sojoji.

Yace, kasancewar abun da rudunar Sojojin Najeriya, tace wai salon yaki yasa suka haura, da kuma cewar zasu dawo, to yanzu idan tace zata hukuta su ta sabawa wance jawabi da ta yiwa duniya, cewar salon yaki ne yasa suka haura.

Ya kara da cewa” in kuwa dama sun gudu ne sakamakon sun kasa tsayawa su fuskaci ‘yan Boko Haram ne, dama dokokin Soja, ta tanadi hukuncin kisa ne ga wanda ya gudu a gaban abokin gaba.”

please wait

No media source currently available

0:00 0:05:46 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG