Hukumomin Siriya sun bayyana a wata rubutacciyar takarda cewa, sojojin gwamnati sun samu dannawa zuwa cikin wasu muhimman yankuna da ke arewa maso gabashin birnin Manbij da ke karkashin Aleppo.
Sojojin na Siriya sun ce su na masu bayar da tabbacin shirin kare dukkannin 'yan Syria da ma daukacin mazauna cikin birnin.
Kungiyar Dakarun kurdawa Masu Kare Siriya (YPG, a takaice) wadda ita ce babbar kungiyar mayakan Kurdawa a Siriya, ta yi kira ga gwamnatin Bashar al-Assad a yau din nan Jumma'a da ta mayar da Manbij a karkashin kulawarta don ta kare yankin daga barazanar hare-hare daga kasar Turkiyya.
"Mu na masu gayyatar gwamnatin Siriya, wadda mu ma wani bangare ne na ta, da ta tura sojojinta don su kwace wadannan wuraren don su kare Manbij daga duk wata barazana daga Turkiyya," a cewar kungiyar ta YPG a takardar bayanin.
Za ku iya son wannan ma
-
Maris 21, 2023
Saudiyya Ta Ce Ranar Alhamis Watan Azumi Zai Kama
-
Maris 17, 2023
Kotun ICC Ta Ba Da Izinin Kama Putin
-
Maris 13, 2023
Shugaba Buhari Ya Taya Xi Jinping Murnar Sake Lashe Zabe