Hukumomin Siriya sun bayyana a wata rubutacciyar takarda cewa, sojojin gwamnati sun samu dannawa zuwa cikin wasu muhimman yankuna da ke arewa maso gabashin birnin Manbij da ke karkashin Aleppo.
Sojojin na Siriya sun ce su na masu bayar da tabbacin shirin kare dukkannin 'yan Syria da ma daukacin mazauna cikin birnin.
Kungiyar Dakarun kurdawa Masu Kare Siriya (YPG, a takaice) wadda ita ce babbar kungiyar mayakan Kurdawa a Siriya, ta yi kira ga gwamnatin Bashar al-Assad a yau din nan Jumma'a da ta mayar da Manbij a karkashin kulawarta don ta kare yankin daga barazanar hare-hare daga kasar Turkiyya.
"Mu na masu gayyatar gwamnatin Siriya, wadda mu ma wani bangare ne na ta, da ta tura sojojinta don su kwace wadannan wuraren don su kare Manbij daga duk wata barazana daga Turkiyya," a cewar kungiyar ta YPG a takardar bayanin.
Za ku iya son wannan ma
-
Janairu 24, 2021
An Ceto Ma'aikata 11 Daga Wata Mahakar Zinari a China
-
Janairu 24, 2021
'Yan Sanda Sun Kama Dubban Masu Zanga Zanga A Rasha
-
Janairu 23, 2021
Adadin Wadanda Suka Kamu Da COVID-19 a Duniya Ya Doshi Miliyan 100
-
Janairu 17, 2021
Wani Ayarin Baki Masu Kaura Na Dosar Amurka Daga Honduras
-
Janairu 16, 2021
India Ta Kaddamar Da Shirin Bada Riga Kafin COVID-19
-
Janairu 11, 2021
WHO Za Ta Aika Wata Tawagar Bincike China