Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Somaliya Ta Shiga Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Gabashin Afirka


Wani taro da kungiyar AEC ta yi a Kenya
Wani taro da kungiyar AEC ta yi a Kenya

Kungiyar mai suna EAC a takaice, na dauke da kasashen Burundi, Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo, Kenya, Rwanda, Sudan ta Kudu, Tanzania da kuma Uganda.

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen gabashin Afirka, ta amince da Somaliya a matsayin sabuwar mamba ta takwas a kungiyar a ranar Juma’a, matakin da hukumomi da ‘yan kasuwar kasar suka ce zai bunkasa fannin tattalin arzikin Somaliya.

Kungiyar mai suna EAC a takaice, na dauke da kasashen Burundi, Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo, Kenya, Rwanda, Sudan ta Kudu, Tanzania da Uganda.

An kafa ta ne a shekarar 2010 kuma tana dauke da kusan mutum miliyan 300 daga kasashen kungiyar.

A wani sakon da ya wallafa a Shafin X da ake kira Twitter a da, Ministan yada labarai da al’adun kasar ta Somalia Daud Aweis, ya ce, kasancewar kasar a wannan kungiyar zai budewa Somaliya hanyoyi na ci gaba da kulla kawance.

Shigar kasar ta Somaliya wannan kungiya a yanzu, ya ba ta damar fadada harkokin kasuwancinta tare da samun kusantar karin gabobin teku da tsawonsu ya kai kilomita 3,000 wadanda za su iya bunkasa harkar samun albarkatun man fetur da iskar gas.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG