Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

SUDAN ta KUDU: Zaman Lafiya Ya Sa Wasu 'Yan Adawa Suka Sa Hannu A Yarjejeniya


Jama'ar Sudan ta Kudu suna murnar yarjejeniyar da aka cimma saboda haka suka fito su tarbi shugaban kasa
Jama'ar Sudan ta Kudu suna murnar yarjejeniyar da aka cimma saboda haka suka fito su tarbi shugaban kasa

Ba duka 'yan bangaren adawa suka amince da abun da yarjejeniyar ta kunsa ba amma sun tabtaba hannu nsu ciki saboda a samu zaman lafiya a kasar ta Sudan ta Kudu

Wasu daga cikin jam’iyyun siyasa na bangaren ‘yan adawa a Sudan ta Kudu, wadanda suka rattaba hannu a wata yarjejeniya da aka kulla a Khartoum, sun ce sun dauki wannan mataki ne saboda a samu wanzuwar zaman lafiya, duk da cewa ba su amince da wasu sharruda da ke kunshe a matsayar da aka cimma ba.

Kungiyar raya kasashen gabashin Afirka ta IGAD, ta fitar da wata sanarwa a jiya Talata, inda ta ce masu shiga tsakanin da suka hada da shugaban Sudan, Omar Al Bashir, za su ci gaba da shimfida hanyoyin tattaunawa, har sai an rattaba hannu a wata yarjejeniyar zaman lafiya mai dorewa.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG