Duk da lafawar da rikicin biyafara ya yi, ana cigaba da tafka muhawara kan ayyana kungiyar Biyafara a matsayin kungiyar ta’addanci da hukumar sojin Najeriya ta yi kwanan baya, duk da ya ke wasu rahotanni na nuna cewa hukumar sojin ta Najeriya ta janye wannan mataki.
Wannan takaddamar kuwa ta yi tsanani ne saboda yadda bangaren gwamnatin Najeriya ya nuna alamar ya na mai ra’ayin cewa ‘yan Biyafaran sun cancanci sunan ‘yan ta’adda kamar yadda sojojin Najeriya su k ace; a yayin da kuma Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya Bukola Saraki ke cewa bai daje a kira ‘yan Biyafara ‘yan ta’adda haka kwatsam ba tare da an tantance tasirin yin hakan ba.
Ganin yadda matsayin Shugaban Majalisar Dattawan ya janyo sukar gaske daga wasu ‘yan Najeriya masu ra’ayin cewa Mr. Nnamdi Kanu da sauran ‘yan kungiyar ‘yan tawayen IPOB ta Biyafara ‘yan ta’adda ne, shugaban Kwamitin Labaru na Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata Aliyu Sahabi, ya ce ba a fahimci manufar Sarakin ba ne. To amma ya bai wa ‘yan Najeriya wadanda su ka fusata da matsayin Sarakin hakuri.
Ga Sale Shehu Ashaka da cikakken labaran:
Facebook Forum