Ana fargabar cewa Tanzania na cike da hadarin samun bullar cutar saboda kwakkwarar huldar kasuwancin da take yi da China, inda tuni hukumomin suka sa ma’aikatan lafiyar kasar cikin shirin ko-ta-kwana.
"Mun dauki karin ma’aikata a tashoshin shiga kasar, sannan muna horar da su kan yadda za su iya gano cutar," a cewar Ministan lafiyar kasar Janeth Mgamba.
Ya zuwa yanzu Ministar ta ce suna da na’urorin gwajin zafin jiki 140 wadanda aka dasa su a filayen tashin jiragen kasar.
Baya ga haka, kwararru a fannin lafiya sun dukufa wajen fadakar da al’umar ta Tanzania kan yadda za su kare kansu daga cutar, inda ake kwadaitar da jama’a da su rike yawan wanke hannayensu da sabulu.
Sannan ana ba da shawarar cewa, idan mutum zai yi tari ko atishawa ya kare bakinsa da kyalle ko wani makari.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 26, 2021
Gwamnatin Nijar Ta Mayar Da Martani Game Da Tarzomar Zabe
-
Fabrairu 25, 2021
An Kama Masu Zanga Zanga Sama Da 200 a Nijar
-
Fabrairu 25, 2021
Ghana Ta Sami Kason Farko Na Rigakafin Coronavirus
-
Fabrairu 23, 2021
NIJAR: Bazoum Mohamed Ya Lashe Zaben Shugaban Kasa
-
Fabrairu 23, 2021
Wai Ko Wa Ake Ganin Zai Lashe Zaben Shugaban Kasa A Nijar?
-
Fabrairu 22, 2021
Ana Jimamin Mutuwar Jami'an Zabe Bakwai Da Suka Rasu a Nijar