Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Taron Kolin Middle Belt Ya Mayarda Martani Akan Matsalolin Najeriya


Pastor Yahanna Burus na Middle Belt Forum.
Pastor Yahanna Burus na Middle Belt Forum.

Al'ummar arewa ta tsakiya ko Middle Belt a taiace sun yi taron koli akan matsalolin da suka addabi Najeriya

A taron sun bada shawarwari akan yadda za'a shawo kan matsalolin.

Taron ya tattaro kananan kabilu daga jihohi goma sha biyar dake shiyar.Sanata Shen Zagbai Nuhu daga jihar Neja shi ne shugaban taron. Yace sun yi taron ne domin su ne ba'a damu dasu ba da irin wahalolin da suke fuskanta. Misali, rashin tsaro su ya fi shafa, su da matansu da 'ya'yansu. Yanzu da zabe ke karatowa yace ba zasu jefawa kowa kuri'a ba sai an yi masu alkawarin cika masu bukatunsu.

Suna bukatan a kula dasu kamar yadda ake kulawa da wasu. Idan an zo sa mutane gwamnati a tabbata an sa mata da maza daga bangarensu. Abu na biyu shi ne batun tsaro.

Tare da tsaro gwamnati ta gyara kasarsu ta kuma inganta rayuwarsu. 'Yan kudu sai su zo kasashensu su fisu kudi domin duk wasu hanyoyi da zasu bi an hanasu. Abubuwan da yakamata a yi masu ba'a yi ba. Na gabansu kuma sun yi gaba. Babu waiwaya baya domin a samu a tafi tare. Suna son matasa su natsu. Su bar shaye-shaye, su kaunaci juna su kuma gayawa junansu gaskiya.

Sun yi korafin an kone masu coci, an kashe masu mutane da jam'an tsaro da suka fito daga cikinsu kuma har yanzu babu abun da gwamnati tayi a kai. Abun da wasu jihohi suke samu a arewa su basa samu. A wannan zabe mai zuwa ba zasu amince da rikicin bayan zabe ba. Wai zasu dakile shi , su hana.

Ga rahoton Zainab Babaji.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:55 0:00
Shiga Kai Tsaye

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG