Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tasirin Babban Taron Tsaro Na Abuja


Sojojin Najeriya da tutar Boko Haram bayan fatattakar 'yan bindigar
Sojojin Najeriya da tutar Boko Haram bayan fatattakar 'yan bindigar

Yayin da ake ta musayar ra'ayi game da hanyoyin yakar Boko Haram, kwararru na ta bayyana muhimmancin wannan taron

Rundunar Sojojin kasashe ma’abuta tafkin Chadi ta ce taron tsaro da kasashen su ka fara yau a babban birnin Tarayyar Najriya Abuja, zai yi tasiri sosai a yakin ta da ‘yan Boko Haram.

Wakilin Muryar Amurka a Abuja da ya turo wannan rahoton Hassan Maina Kaina, ya lura cewa wannan taron wani dori kan abubuwan da aka cimma taron da kasashen su ka yi a birnin Paris a baya, ciki har da batun yinkurin kwato ‘yan matan Chibok.

Kakakin Rundunar kasashe ma’abuta yankin na Chadi, Kanar Muhammed Dole ya gaya ma wakilinmu Hassan cewa ga dukkan alamu za a kara ba ma rundunar goyon baya a yakin da ta ke yi da Boko Haram. Haka zalika, hukumar raya yankin tafkin Chadi ta bukaci da a mai da hankali kan abubuwan da za su kawo farfadowa da kuma bunkasa yankin na Tafkin Chadi.

Ga wakilinmu Hassan Maina Kaina da cikakken rahoton:

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:06 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG