Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tattalin Arziki: Hukumomin Najeriya Sun Fara Mai Da Hankali Kan Bangaren Da Ba Na Man Fetur Ba


Hedikwatar NNPC da ke Abuja, Najeriya
Hedikwatar NNPC da ke Abuja, Najeriya

Yayin da annobar corona ke cigaba da durkusar da ayyukan yau da kullum a fadin duniya, Najeriya ta fara fuskantar barazana a fannin tattalin arziki, inda tasirin faduwar farashin danyen mai ya sa gwamnatin tarayyar kasar ta fara nuna damuwa kan yadda gwamnatocin jihohi za su iya cigaba da biyan albashin ma’aikata a matakai daban-daban.

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta fara daukar matakan bunkasa tattalin arzikin kasar ganin yadda annobar corona ke cigaba da yin barazana ga harkokin kasuwanci, inda ta fara zuba jari a bangaren cinikin albarkatun man fetur ta kan tudu a kasar.

A matakin jihohi, gwamnan jihar yobe, Mai Mala Buni, ya bayyana cewa tun da gwamnatinsa ta dare karagar mulki, an bada himma wajen tuntubar kwararru a fannin aikin noma domin karkatar da tattalin arzikin jihar saboda a samawa al’umar karkara ayyukan yi su dogaro da kai.

Kayan Amfanin Gona
Kayan Amfanin Gona

Ya kara da cewa, samun man fetur ya gurgunta aikin noma.

Kazalika, gwamna Mai Mala Buni ya ce gwamnatoci na shawara a kan bullo da dabarun tabbatar da cewa ana biyan albashin ma’aikata a lokacin da ya kamata.

Daga karshe dai, Mai Mala ya ce gwamnatinsa ta ayyana dokar ta baci a fannin ilmi, kuma kwararru na aiki domin farfado da bangaren ilmin.

Ga Halima Abdulrauf da cikakken rahoton:

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:44 0:00


Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG